Ƙungiyar Kwankwasiyya Movement, ta sanar da cewa Mataimakin gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya miƙa takardar murabus daga mukaminsa a yau Juma’a.
Sanarwar ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne duk da wahalarsa, domin kare muradun al’ummar jihar da kuma tabbatar da daidaito da kwanciyar hankali a harkokin mulki.
Ta ƙara da cewa wasu halin da ake ciki a baya-bayan nan sun takaita cikakken aiwatar da ayyuka da alhakin ofishin mataimakin gwamna, lamarin da ya sa ya zama dole a bar kujerar domin ta samu damar gudanar da aikinta yadda ya kamata.
Sai dai an jaddada cewa murabus ɗin ba yana nufin amincewa da zarge-zargen da Majalisar Dokokin Kano ta yi masa ba, inda ya ci gaba da jaddada cewa yana da tsabta kuma aikinsa na baya shaida ne kan gaskiyarsa da jajircewarsa.
Ƙungiyar ta kuma ce Gwarzo zai mayar da hankali wajen ƙarfafa harkokin Kwankwasiyya Movement da sake tsara manufofinta gabanin zaɓen 2027, tare da kira ga al’umma da su kasance masu natsuwa, bin doka da oda, da kuma ci gaba da mara wa manufofin nagartaccen shugabanci baya.













































