Yanzu-Yanzu: JAMB ta rike maki 150 a matsayin mafi karanci domin shiga jami’a

Jamb 1 1

Hukumar Shiga Jami’a da Jarrabawar Shiga Manyan Makarantun gaba da Sakandire(JAMB) a bana ma ta amince da maki 150 a matsayin mafi karancin maki na shiga jami’o’in Najeriya a zangon karatu na shekarar 2026/27.

An sanar da wannan hukuncin ne a ranar Litinin a taron da hukumar ke yi na shekara-shekara na kan samun gurbin karatu da aka gudanar a Abuja, inda manyan masu ruwa da tsaki a fannin ilimi suka tattauna kan sharudan samun gurbin karatu a manyan makarantu a fadin kasar.

A cewar hukumar ta JAMB, an amince da wannan matsayar bayan tattaunawa da zabe da shugabannin jami’o’i da sauran shugabannin cibiyoyin ilimi da suka halarci taron suka yi.

A karkashin sabon tsarin, ana sa ran jami’o’i a fadin Najeriya za su karbi daliban da suka samu akalla maki 150 a Jarrabawar UTME.

Hukumar ta kuma amince da maki 150 a matsayin mafi karancin maki na shiga Kwalejojin Kiwon Lafiya, yayin da Kwalejojin Fasaha za su karbi daliban da suka samu akalla maki 100.

Taron, wanda JAMB ke gudanarwa kowace shekara, wuri ne da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi ke tantance yadda za a gudanar da hanyoyin da dalibai za su samu guraben karatu da maki, da sauran bukatu don zangon karatu mai zuwa.

Makin da JAMB ta sanar na wakiltar mafi karancin na shiga jami’a, duk da cewa kowace cibiya tana da ‘yancin sanya mafi girma dangane da yadda shirinta ke da gasa.

Hukumar ta bayyana cewa an cimma matsaya kan wadannan batutuwan ne bayan tattaunawa mai zurfi da nufin daidaita samun damar ilimi mafi girma da bukatar kiyaye matsayin karatu.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da gyare-gyare a tsarin shigar daliban Najeriya, ciki har da sabbin shawarwarin cewa wasu daliban da ke neman shiga shirye-shiryen ilimi da noma ba za su zauna UTME ba karkashin wasu sharudda.

A ‘yan shekarun nan, jami’o’in da ke da shirye-shiryen da ke da gasa sosai kamar Magani, Shari’a, Harhada Magunguna, da Injiniya yawanci suna sanya matakan shiga da ya fi mafi karancin da JAMB ta amince da shi.

Ana sa ran daliban da ke neman shiga manyan makarantu a zangon karatu na shekarar 2026/27 za su fara shirye-shirye bisa sabbin ka’idojin da aka amince da su.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here