Jami’an tsaron jihar Ondo Amotekun, sun kama wadan da ake zargi suna da hannu wajen harin da aka kai cocin jihar Ondo.
kumandan ‘yan Amotekun na jihar, Adetunji Adeleye, ne ya bayyana hakan yayin shelan wadan da ake zargin yau Alhamis a Akure.
Ya ce sun gano makamai da kuma motocin da akai amfani dasu wajen kai harin.
Sama da mutane 40 sun rasa rayukansu kansu yayin da sama da mutum 70 suka jikkata yayin kai harin a ranar 5 ga watan June na shekarar 2022.
Munan tafe da karin bayani













































