Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA ta bukaci masu amfani da hanya musamman direbobi da su kasance masu hakuri da yin tuki a cikin natsuwa a watan Ramadan.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na KAROTA, Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa ya fitar a ranar Alhamis din nan, ya ce watan Ramadan lokacin ibada ne da ke kawo sauye-sauyen halayen tuki sakamakon kasala, rashin wadataccen ruwa a jiki, da yawan cunkoson ababen hawa, musamman a lokutan buda baki da tarawihi.
SolaceBase ta ruwaito cewa sanarwar ta ce domin tabbatar da tsaron lafiyar kowa da kowa a kan tituna, KAROTA ta shawarci direbobi da su bi wadannan ka’idoji a cikin watan Ramadan:
Karin karatu: KAROTA ta kama jabun magungunan kashe qwari da kuma magungunan da wa’addin amfani da su ya kare na sama da miliyan 30
A guji yawan Gudu kafin buda baki – Wasu direbobin kan garzaya gida domin yin buda baki, abin da ke haifar da cunkoson ababen hawa da hadurra, don haka dirbobi su i tuƙi a cikin aminci don kare kansu da sauran jama’a.
Kasance cikin Fadakarwa da Natsuwa – Azumi na iya haifar da gajiya ko juwa, a don haka KAROTA ta shawarci direbobi idan sun ji gajiya ko barci, u huta kafin ku ci gaba da tafiya.
Yin Haƙuri da Ladabi akan Hanya – Cunkoson ababen hawa na ƙaruwa, musamman a kusa da kasuwanni da masallatai. Direbobi su gujewa tuƙi da ganganci kuma nuna ƙosawa da rashin fahimta ga wasu.
Yawaita shan ruwa da cin abinci mara nauyi kafin Tuƙi – Tabbatar sa cewa direbobi sun sha isasshen ruwa kuma sun ci abinci mai sauƙi a lokacin Suhoor don kula da kuzari da mayar da hankali yayin tuki.
Kula da masu tafiya a ƙasa da masu keke – Mutane da yawa suna tafiya zuwa masallatai, musamman da dare. Direbobi su yi tuƙi a hankali, musamman a wuraren cunkoso.
Shirya shiryen fita a kan lokaci – Idan zai yiwu, ku guje wa tafiya a lokutan cunkoso da yawa kuma ku tuƙi lokacin da kuke cikin yanayi mai kyau.
Bin dokokin tafiya da amfani da umurnin jami’an KAROTA – Direbobi su kasance sun yi gudu daidai yadda aka umarta, tare da bin dokokin zirga-zirga don kare rayuwar su da ta wasu.
A cewar KAROTA za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron tituna a cikin watan Ramadan kuma za ta kara yawan sintiri domin saukaka zirga-zirgar ababen hawa.
A don haka ta yi kira ga dukkan direbobi su rungumi hakuri, su mutunta juna, su yi tukin nutuswa a cikin wannan wata mai alfarma.
Shugaban hukumar KAROTA Faisal Mahmud Kabir yana yiwa kowa da kowa fatan alkairi da kuma fatan Allah ya bamu lafiya da zaman lafiya.













































