Yanzu Yanzu: Shugaban Kasa Tinubu Ya Dakatar Da Emefiele 

IMG 20230605 WA0003 1 750x430 1
IMG 20230605 WA0003 1 750x430 1

Labari da ke zuwa mana a yanzu haka ya kawo cewa shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Godwin Emefiele a matsayin gwamnan babban bankin Najeriya (CBN).

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan labarai na ofishin babban sakataren gwamnatin tarayya, Willie Bassey ya fitar a yau Juma’a, 9 ga watan Yuni, Channels TV ta rahoto.

Ya ce: “Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da gwamnan babban bankin Najeriya, Mista Godwin Emefiele, CFR, daga ofis nan take.”

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here