Da Mun Hadu Da Kwankwaso Da Na Dalla Masa Mari — Ganduje

Ganduje sad
Ganduje sad

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce da sun hadu da  takwaransa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a Villa da ya dalla masa mari.

Dr Ganduje ya bayyana haka ne da yammacin Juma’a a Fadar shugaban kasa dake Abuja.

Ya ce ya je Villa ne kai karar Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf kan yadda yake rushe gine-gine a wuraren da shi Gandujen ya bayar a zamanin  mulkinsa.

Ya na cikin Villa ne kuma Sanata Rabiu Kwankwaso suka shiga tattaunawar sirri da shugaban kasa Bola Tinubu.

Wannan ce ta sa Dr Ganduje ya bayyana takaicinsa da zuwan Sanata Kwankwason.

“Bamu hadu da shi ba, amma da na gan shi da zan iya kantsa masa mari saboda barnar da ya kawo a Kano” in ji Ganduje.

(Aminiya )

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here