Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Kasa da Tsara Birane ta Jihar Kano, ta gayyaci jama’ar da suka sayi filaye a Gandun Sarki Sabon Gida da ke Panisau, Karamar Hukumar Ungogo, ta hannun Kamfanin Aminci Micro-Credit Company, da su zo domin tantancewa biyo bayan tsara filin da gwamnati ta yi a yankin.
Sanarwar, wadda Jami’in Hulda da Jama’a na rkon kwarya na Hukumar, Isah Mansur Bello, ya sanya wa hannu a ranar Juma’a, ta ce wannan aikin na daga cikin kokarin tabbatar da tsare-tsaren takardu daidai da biyan diyya ga masu filayen da lamarin ya shafa.
Bello ya bayyana cewa za a kula da mutanen da ke da ingantacciyar shaidar mallaka kawai, yana mai rokon su da su hada kai da jami’ai a duk lokacin aikin.
A cewar sanarwar, duk masu ruwa da tsaki ana bukatar su je ofishin Hukumar da ke kan titin Sabo Bakin Zuwo, kusa da Gidan Gwamnatin Jihar Kano, da takardun mallakar su domin tantancewa da sarrafa biyan diyya.
Hukumar ta ce za a fara aikin tantancewa a ranar Litinin, 11 ga Mayu, 2026, kuma zai gudana kowace rana daga karfe 9:00 na safe zuwa 4:00 na yamma, tana mai jaddada mahimmancin biyayya cikin gaggawa.
“Ana shawartar jama’a da su yi komai cikin tsari da doka yadda ya dace,” in ji sanarwar.











































