NLC: Yajin aikin kungiyoyin kwadago ya shafi Kano yayin da bankuna da makarantu ke rufe

NLC, yajin aikin, kungiyoyin, kwadago, Kano, bankuna, makarantu, rufe
Yajin aikin da kungiyoyin kwadago suka yi a fadin Najeriya ya samu gagarumar nasara a Kano ranar Litinin yayin da bankuna da ma’aikatan gwamnati da...

Daga: Sunusi A. Dantalata Fagge

Yajin aikin da kungiyoyin kwadago suka yi a fadin Najeriya ya samu gagarumar nasara a Kano ranar Litinin yayin da bankuna da ma’aikatan gwamnati da ma’aikatan jirgi suka kauracewa aiki.

Makarantu masu zaman kansu sun kasance a cikin zaman yayin da ma’aikatansu suka bijirewa umarnin yajin aikin da kungiyoyin kwadago karkashin jagorancin NLC da TUC suka yi.

Karin labari: Ƙungiyar ƴan jarida ta Najeriya ta bi sahun yajin aikin ƙwadago

Wakilin NAN da ya bi diddigin lamarin ya rawaito cewa an rufe kofofin bankuna da sauransu.

Matakin jaha da na tarayya na rufe, an lura cewa ma’aikatan tarayya ba sa aiki an ga irin wannan yanayin a rukunin sakatariyar Audu Bako da ke Kano.

Sakatariyar gwamnatin tarayya ce ta kunshi hukumar kula da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NAFDAC) da sauran ma’aikatu da hukumomi.

Karin labari: Mafi Karancin Albashi: ASUU ta shiga yajin aikin gama gari

A filin jirgin sama na Malam Aminu Kano babu tashin jirage sai masu tashi zuwa kasa mai tsarki don gudanar da aikin hajji.

Wasu ma’aikatan makarantu masu zaman kansu sun shaidawa manema labarai cewa ba sa cikin yajin aikin saboda sabon mafi karancin albashi ba zai shafe su ba idan har gwamnatin tarayya ta amince da su.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here