Karamin ministan kwadago da ayyuka, na Najeriya mai barin-gado, Festus Keyamo (SAN), ya gaya wa Shugaba Muhammadu Buhari mai barin-gado cewa nada mukamin karamin minista ya saba wa tsarin mulkin kasar.
Keyamo wanda babban lauya ne a Najeriya ya fadi hakan ne a jiya Laraba, lokacin da yake gabatar da jawabinsa a zaman majalisar zartarwa na ban-kwana domin kawo karshen majalisar, wanda Shugaba Buhari ya jagoranta a Abuja.
Karamin ministan ya nuna cewa wannan mukami da ake bai wa mutane yawanci da sunan gwamnatin hadin kan kasa kusan ba ya aiki a zahiri ga yawancin wadanda ake nadawa a matsayin.
Domin ba wani iko na a-zo-a-gani da suke da shi lamarin da a wani lokacin ma yake hada su rigima da wanda yake matsayin ainahin matsayin ministan.
Ya ce yawancin wadanda gwamnatocin baya suka nada wa a wannan mukami sun ki fitowa su yi magana ne saboda kar a ga ba su gode wa Shugabannin kasar da suka ba su mukamin ba.
Festus Keyamo shi ne kakakin rusasshen kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu da Shettima.













































