Majalisar dattawa a ranar Laraba ta tabbatar da nadin Nnamonso Ekanem da Mahmoud Abubakar Magaji a matsayin mambobin hukumar kula da harkokin shari’a ta tarayya.
Wadanda aka nada wadanda suka fito daga Akwa-Ibom da Neja su ne za su wakilci shiyyar Kudu-maso-Kudu da shiyyar Arewa ta Tsakiya a Hukumar.
Tabbatar da mutanen biyu ya biyo bayan nazarin rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin shari’a da kare hakkin bil’adama da shari’a, wanea Sanata Opeyemi Bamidele yake jagoranta.
Bamidele, a jawabinsa, ya ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya gabatar da sunayensu kamar yadda sashi na 154, karamin sashe na (1) da (3) ya yi daidai da sakin layi na 12 (e) na Jadawali na uku na kundin tsarin mulkin 1999.
A cewar dan majalisar, wadanda aka nada “sun dace da zama a matsayin mambobin hukumar kula da shari’a ta tarayya”.
Ya bayyana cewa babu wasu korafe korafe ko rahoto kan wadanda aka nada, inda ya kara da cewa “binciken da aka yi da kuma wasu nau’ikan binciken da hukumomin tsaro suka yi bai nuna wata mummunar alaka a kansu ba.”
Bamidele ya bayyana gamsuwa da cancanta, gogewa, kwarewa da amincin wadanda aka zaba a matsayin mambobin hukumar.
A wani labarin kuma, Majalisar Dattawa ta mika bukatar Buhari na amincewa da sunayen mutane hudu da aka nada a matsayin kwamishinonin hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya NERC ga kwamitin kula da wutar lantarki.
Wadanda aka zaba za su bayyana a gaban kwamitin domin tantancewa sun hada da Dr Yusuf Ali (Arewa Ta Tsakiya), Mista Chidi Ike (Kudu maso Gabas), Mista Nathan Shatti (Arewa Maso Gabas) da Mista Dafe Akpeneye (Kudu Kudu).
Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya ba wa Kwamitin wa’adin makonni biyu da ya kawo rahoto a zauren majalisar.













































