Kwankwaso ya bayyana kansa a matsayin ɗan siyasa mai daraja ta musamman a Kano yayin da rikici ke ƙara kamari tsakaninsa da Gwamna Abba

Rabiu Kwankwaso 2 750x430

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya kuma tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana kansa a matsayin ɗan siyasa ɗaya tilo a Jihar Kano da ba a iya siye da kuɗi.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa Kwankwaso, wanda ya kasance ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen gama gari na shekarar 2023, ya bayyana cewa kuɗi ba su da tasiri a kan matsayinsa da shawarar siyasarsa.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da magoya bayan Kwankwasiyya a gidansa da ke Kano, inda ya nuna cewa duk da yadda mutane da dama ke ganin babu ɗan siyasa da ba za a iya rinjaya shi da kuɗi ba, shi yana alfahari da kasancewa mutum mai daraja ta musamman da ba a iya saya.

Kwankwaso ya ƙara da cewa idan burinsa kuɗi ne, ya san inda ya kamata ya daidaita kansa a siyasa, yana mai nuni da cewa babu wani lokaci da aka taɓa zuwa wajensa da tayin a rinjaye shi ko a siye matsayinsa na siyasa.

Ya kuma faɗaɗa wannan siffa zuwa ga magoya bayansa, inda ya bayyana cewa mabiya Kwankwasiyya ma su na da irin wannan daraja ta musamman, domin ba su yarda kuɗi su rinjaye su a lokacin zaɓe.

Sanatan ya yi kira ga magoya bayansa da su kasance masu natsuwa da haƙuri, yana mai tuna musu cewa dukkan mukaman siyasa na wucin gadi ne, kuma Allah na da ikon sauya kowane hali a kowane lokaci.

Wannan furuci na Kwankwaso na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun rahotanni game da ƙara tsanantar rashin jituwa tsakaninsa da tsohon yaronsa a siyasa, Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf, sakamakon jita-jitar da ke yawo cewa gwamnan na shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here