Kayyade kudaden da za a cire a kullum zai fi shafar ‘yan siyasa ba talakawa ba – Sanusi II

IMG ORG 1597051154134
IMG ORG 1597051154134

Khalifa Muhammad Sanusi , ya ce matakin da babban bankin Najeriya ya dauka na takaita cirar kudaden zai fi yin tasiri a kan `yan siyasa kasar fiye da talakawa.

Ya bayyana hakan ne a karshen karatun Madaris da ya saba yi duk karshen mako.

Ya ce `yan siyasar kasar na amfani da kudi a lokacin zabe don sayen kuri’un jama’a, lamarin da ke haifar da koma-baya ga kasar.

Muhammadu Sanusi na II ya ce “abin takaici ne yadda mutane za su yi shekara hudu suna kwasar dukiyar al’umma, suna barin mutane a cikin wahala da yunwa, sannan su fito da irin kudaden su sayi kuri’u, su biya ‘yan sanda, da DSS, da ma’aikatan INEC da `yan daba a sayo musu kwaya, a saya musu makamai, don hana mutane zabe.”

Haka kuma tsohon Sarkin na Kano ya ce wannan tsari da CBN ya fito da shi shi ne zai fara rage barnar da ‘yan siyasa ke yi kuma zai takaita magudin zabe.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here