Za a gudanar da bikin rantsar da sabon shugaban Jami’ar Tarayya ta Dutse da ke Jihar Jigawa, Farfesa Ahmad Mohammed Gumel, kamar yadda aka tsara, a ranar 10 ga watan Fabrairu, bayan an tabbatar da cikar dukkan matakan da doka ta tanada wajen zaɓensa.
Hakan na cikin jaridar FUD Newsletter a wata tattaunawa da Barista Shamsu Ubale Jubrin, Lauyan wanda ake kara (Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Tarayya da wasu 22) a karar da Farfesa Abdulsalam Balarebe, daya daga cikin masu neman mukamin shugaban jami’ar, ta hannun lauyansa, yana kalubalantar tsarin zaben da kuma rokon kotun da ta hukunta duk wanda ake tuhuma da gabatar da karar da bikin mika mulki ga sabon mataimakin shugaban kasa.
Jaridar Solacebase ta rawaito cewa lauyan ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi tare da takardu a gaban kotu, inda ya nuna cewa an kammala tsarin zaɓen shugaban jami’ar ba tare da karya ka’idojin cancanta da aka wallafa a jaridun ƙasa ba.
Ya bayyana cewa lauyan Farfesa Abdulsalam Balarebe bai gabatar da wata hujja a gaban kotu da ke nuna cewa ba a bi ka’idojin da suka dace wajen naɗin sabon shugaban jami’ar ba.
Hujjojin da aka gabatar sun nuna cewa Farfesa Gumel ya cika dukkan sharuddan naɗin mukamin, inda ya samu mafi girman maki tare da zama na farko a ƙarshen tantancewa, lamarin da ya sa majalisar gudanarwar jami’ar ta naɗa shi a matsayin shugaban jami’ar na huɗu a cikinta.
Kotun ta ƙi amincewa da buƙatar hana gudanar da bikin rantsarwa, inda ta ɗage sauraron shari’ar zuwa wani lokaci bayan bikin, abin da aka bayyana a matsayin nasara ta fasaha ga majalisar gudanarwar jami’ar da kuma Farfesa Gumel.












































