Dubban muminai ne suka halarci gudanar da Sallar Idi a fadar mai martaba Sarkin Kano Aminu Ado Bayero a fadarsa ta Nassarawa da ke Kano, a daidai lokacin da aka kammala azumin watan Ramadan.

Sallar wadda Malam Kamalu Sarkin Malamai ya jagoranta, ta tabo batun jagoranci da tsarkake zuciya.

A cikin hudubarsa, Malam Kamalu ya gabatar da wani sako mai inganci, inda ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su kiyaye da dabi’un hakuri da godiya da ake koya a cikin watan Ramadan.
Ya kuma jaddada yanayin rayuwar duniya ta wucin gadi, inda ya bukaci masu ibada da su dage da ayyukan alheri fiye da watan mai alfarma.













































