Gwamnatin Katsina ta janye haramta ayyukan sadarwa

telecoms masts in Nigeria
telecoms masts in Nigeria

Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari, ya rubutawa hukumar sadarwa ta Najeriya NCC wasiƙar buƙatar dawo da ayyukan layukan wayar salula a ƙananan hukumomi 10 daga cikin 17 da aka dakatar da sadarwar watanni huɗu da suka gabata.

Solacebase ta ruwaito cewa ƙananan hukumomi goma da abin ya shafa sun haɗa da Kurfi da Dutsinma da Matazu da Musawa sai Malumfashi da Dandume da  Bakori da Funtua da ƙaramar hukumar Kafur da kuma Danja.

Ƙananan hukumomin da dawo da harkokin sadarwar bai shafa ba sun haɗa da Faskari da Sabuwa da Batsari sai Safana da Kankara da Danmusa da kuma ƙaramar hukumar Jibia.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yaɗa labaran gwamnanAbdu Labaran Malumfashi, ya fitar a Alhamis ɗin makon nan.

Idan za a iya tunawa, gwamnatin jihar Katsina ta zartar da dokar hana aikata laifuka, wanda baya ga dakatar da ayyukan wayar da kan jama’a a ƙananan hukumomi 17, ta kuma haramta amfani da wasu hanyoyi a yankunan da abin ya shafa, da safarar itace a cikin jihar, da sayar wa kowa da kowa nau’o’in dabbobi a ciki, da kuma rufe wasu manyan kasuwanni a wuraren da abin ya shafa da kuma sayar da babura a kasuwannin da abin ya shafa da kuma hana amfani da baburan haya daga ƙarfe 10:00 na dare zuwa karfe 5:30 na safe a fadin jihar da sauransu.

”Hukuncin da gwamnati ta yanke na dakatar da dokar a ƙananan hukumomi goma ya biyo bayan dawowar al’amuran yau da kullum, duk da cewa an ci gaba da kokarin ganin an samu zaman lafiya a kowane bangare na jihar”. ‘ in ji sanarwar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here