Gwamnatin jihar Katsina ta bayar da umarnin dakatar da shugaban sashin kula da gandun daji na karamar hukumar Malumfashi da ke jihar nan take.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labaran Gwamnan, Alhaji Aliyu Yaradua ya sanya wa hannu a madadin Sakataren Gwamnatin Jihar.
Sanarwar ta ce hakan ya biyo bayan zargin shugaban na sayar da sassan dajin Makaurachi da ke yankin karamar hukumar.
Karanta wannan: Rundunar Sojin sama ta yi Karin girma ga jami’anta
Gwamna Dikko Radda ya kuma umarci hukumar karamar hukumar da ta zakulo duk wasu jami’an da ke da hannu a cikin wannan badakala.
Sanarwar ta kara da cewa, “Sunan Usman Illiyasu ya yi fice a cikin haramtattun harkalloli.
An kuma umarci hukumar karamar hukumar da ta yi bincike tare da kai rahoto ga gwamnan.













































