Hukumar kula da Filayen Jiragen Sama ta ƙasa ta sanar da jama’a tashin gobara a Sashen Farko na Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas.
Sanarwar ta fito ne ta shafin sadarwar zamani na hukuma a ranar Litinin.
Hukumar ta ce tawagar kashe gobara nata aiki domin dakile yaduwar gobarar tare da shawo kan lamarin, kuma babu asarar rai da aka samu zuwa yanzu.
Ta kara da cewa za a ci gaba da sanar da jama’a karin bayani yayin da ake samun sabbin bayanai.
Rahotanni sun nuna cewa an ga hayaki mai yawa tare da rudani a sashen jiragen a farkon ranar Litinin.
Ayyukan ceto na gaggawa na ci gaba da gudana yayin da tawagar jami’an kashe gobara ke kokarin shawo kan gobarar gaba daya, tare da fitar da fasinjoji da ma’aikatan filin jirgin cikin tsari.
Hukumar ta ce domin karfafa kokarin dakile gobarar, an nemi karin tallafi daga Gwamnatin Jihar Legas, kamfanin Julius Berger Nigeria Plc, kamfanin China Civil Engineering Construction Corporation, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, da sauran hukumomin agaji masu alaka.
Hukumar ta jaddada cewa babu asarar rai da aka samu zuwa wannan lokaci, kuma ana daukar dukkan matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyi.
Za a ci gaba da fitar da sahihan bayanai yayin da ake samun ci gaba kan lamarin.













































