Allah ya yi wa manajan daraktan hukumar kwashe shara ta jihar Kano REMASAB Haruna Danzago rasuwa.
Majiya daga ‘yan uwansa tace ya rasu ne a safiyar ranar Alhamis a asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH) bayan ya sha fama da rashin lafiya.
Danzago, ma’aikacin gwamnati ne, kuma dan siyasa mara tsoro, ya shahara da irin gudunmawar da yake bayarwa a harkokin siyasa a jihar Kano.
Gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya nada shi a matsayin Manajan Daraktan REMASAB a ranar 5 ga Yulin, 2023.
Majiyoyi sun ce za a yi jana’izar sa a kofar Kudu, fadar Sarkin Kano.













































