Fitaccen malamin addinin musulunci kuma jagora a ƙasar nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu bayan doguwar jinya.
Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu da safiyar ranar Alhamis a Cibiyar Koyarwa ta Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi.
Wani ɗan uwan marigayin mai suna Malam Ahmed Mohammed ya tabbatar da rasuwar a Bauchi, inda ya bayyana cewa malam ya karɓi baƙi har daren Laraba kafin daga bisani a kaishe shi asibiti inda ya rasu.
A cewar iyalan, za a gudanar da sallar jana’izar marigayin a ranar Juma’a, 28 ga Nuwamba, a Bauchi bisa tsarin shari’ar musulunci.
Sheikh Usman-Bauchi, wanda mai rikon lambar girmamawa ta (OFR) ne, ya shahara a Najeriya saboda zurfin iliminsa, jagorancinsa da jajircewarsa wajen yaɗa addinin musulunci cikin lumana da fahimtar juna.
An haife shi a shekarar 1927 a Gombe, kuma ya sadaukar da rayuwarsa wajen inganta ilimin musulunci, ƙarfafa zaman lafiya da haɓaka haɗin kai a ƙasar nan, tare da jagorantar ƙungiyar Tijjaniyya a Najeriya.
Marigayin ya taka muhimmiyar rawa a ci gaban al’umma, tarbiyyar matasan malamai da kuma bunƙasa fahimtar addini, sannan ya bar ’ya’ya 61 da kuma jikoki da ƴaƴan jikoki da dama.
NAN













































