Cikin Hotuna: Mataimakin gwamnan Kano, Kwamishinoni masu biyayya ga ɓangaren Kwankwaso sun halarci taron majalisar zartarwa a yayin da rikicin siyasa ke ƙara ƙamari

WhatsApp Image 2026 01 16 at 17.33.51 750x430

A yayin da rikicin siyasa ke ci gaba da ƙamari a jihar Kano, mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Gwarzo, tare da wasu kwamishinoni da ake danganta su da biyayya ga tsagin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, sun bayyana a taron majalisar zartarwar gwamnati da ke gudana a Abuja ranar Juma’a.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa daga cikin kwamishinonin da aka gani a taron akwai Mustapha Kwankwaso ɗan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Yusuf Kofar Mata, da wasu manyan kusoshin siyasa da ke kusa da tsohon gwamnan Kano, a daidai lokacin da ake fama da tsananin rikici tsakanin gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da jagoransa na siyasa Rabiu Musa Kwankwaso.

Bayyanar su a taron ta ƙara tayar da jita-jita kan zurfin rabuwar kai da ke kara bayyana a cikin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party a jihar Kano.

Rikicin siyasar na da alaƙa da rahotannin da ke nuna cewa gwamna Abba Kabir Yusuf na shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC, lamarin da ya girgiza tsarin siyasar Kwankwasiyya wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasararsa a zaɓen gwamna.

Yanayin da ake ciki ya ƙara nuna alamun rikice-rikice da rashin jituwa a cikin jam’iyya mai mulki, yayin da ake ci gaba da jiran yadda wannan rikici zai ƙare da kuma tasirinsa ga tafiyar siyasar jihar Kano.

Hotunan da aka wallafa sun nuna mataimakin gwamnan da kwamishinonin sun halarci taron majalisar zartarwa, abin da ya jawo hankalin jama’a da masu sharhi kan siyasa game da abin da hakan ke nufi a halin da ake ciki na rikicin siyasa a jihar.

WhatsApp Image 2026 01 16 at 17.33.49 768x960 WhatsApp Image 2026 01 16 at 17.33.50 768x576

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here