Babban lauyan gwamnatin tarayya ya caccaki Majalisar dokokin jihar Edo kan dakatarwar da aka yi wa shugabannin kananan hukumomi

fagbemi lateef 1

Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi, SAN, ya bayyana dakatarwar da aka yi wa Shugabanni da mataimakan shugabannin kananan hukumomin 18 a Jihar Edo a matsayin haramtacce kuma ba bisa ka’ida ba.

AGF wanda ya zanta da manema labarai a Abuja ranar Alhamis ya jaddada cewa tsige su daga mukaminsa ko kuma dakatar da duk wani zababben jami’in LG a kasar nan ba hakkin ‘yan majalisa ne ba.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here