Gwamnatin Osun ta bayar da umarnin gudanar da bincike kan zargin sanya guba a abincin wasu daliban Firamare 18

Ademola Adeleke
Ademola Adeleke

Gwamnatin Osun ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin sanya guba a abincin wasu dalibai 18 a makarantar firamare ta St. James (B) Owoope da ke Osogbo.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar Kolapo Alimi ya fitar aka rabawa manema labarai ranar Talata a Osogbo.

Sanarwar ta ce Gwamna Ademola Adeleke shi ne ya ba da umarnin gudanar da binciken tare kuma da daina dafa abincin.

Sanarwar tace an gayyaci masu dafa abinci a makarantar da jami’in dake kula da su domin amsa tambayoyi a Talatar nan.

Karanta wannan:Kamfanin samar da wutar lantarki na Najeriya ya gyara wutar bayan da ta katse a ranar litinin  

A cewar sanarwar, gwamnatin jihar ta biya duk wasu kudade na duba lafiyar daliban bayan an sallame su daga wani asibiti da ba a bayyana ba.

Shugaban Hukumar Ilimin bai daya na jihar, Mista Nathaniel Ojetola, ya ce an yi wa dalibai 18 jinya tare da sallamar su.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here