Akalla Naira miliyan 800 aka biya ga ‘yan ta’addan da suka sace fasinjojin jirgin AK9 da aka kai wa hari a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, kafin a sako mutane 7 dake hannun su a ranar Asabar, kamar yadda wasu iyalan wadanda abin ya shafa da wasu majiyoyin da ke da masaniya kan yarjejeniyar suka shaida wa Aminiya ranar Lahadi.
A ranar Talata dai, Aminiya ta ruwaito cewa wadanda suka yi garkuwa da fasinjojin jirgin sun aika da wani faifan bidiyo ga iyalan wadanda abin ya shafa suna barazanar kashe wadanda aka kama idan iyalan ba suka saba yarjjeniyar.
An tattaro cewa iyalan kowane daya daga cikin ‘yan Najeriya shida da aka kashe sun biya Naira miliyan 100 yayin da masu garkuwa da su suka yi zargin kudin fansar dan Pakistan din a kan Naira miliyan 200 da kuma aka biya.
“N200 miliyan ne kawai aka tara a Naira, sauran Naira miliyan 600 kuma an biya kwatankwacin dalar Amurka,” in ji daya daga cikin majiyar mu.
Wadanda aka saki sun hada da Muhammad Daiyabu Paki, Bosede Olurotimi, Abubakar Zubairu, Alhassan Sule, Sadiq Ango Abdullahi, Aliyu Usman da Muhammad Abuzar Afzal dan kasar Pakistan.













































