Alhassan Doguwa Ya Lashe Zaben Majalisar Tarayya Karo Na Biyar

Alhassan Ado Doguwa.jpeg
Alhassan Ado Doguwa.jpeg

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Honarabul Alhassan Ado Doguwa, ya lashe zaben dan Majalisar Tarayya mai wakilatar Kananan Hukumomin Doguwa da Tudun Wada na Jihar Kano.

Tun a shekarar 2007 Honarabul Doguwa ya shiga zauren majalisar, inda a yanzu ya zamana cewa ya lashe zaben kujerar karo na biyar a matsayin mai wakiltar kananan hukumomin Doguwa da Tudun Wada a matakin Tarayya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here