Hukumar da ke Kula da Cututtuka ta Jihar Kano (KSACA) ta fara gudanar da gwajin lafiya kafin aure ga mutane 3,000 ma’aurata da aka zaba a shirin auren gata na gwamnatin jihar na 2026.
Jami’an da ke kula da aikin sun jaddada cewa wadanda suka cancanta ta fannin lafiya ne kawai za su amfana da shirin.
SolaceBase ta ruwaito cewa ana gudanar da gwajin ne a hedkwatar hukumar da ke Na’ibawa, karamar hukumar Kumbotso, inda ake duba cuta mai karya garkuwar jiki (HIV), ciwon hanta, zazzabin cizon sauro na (syphilis) da cutar gado ta (sickle cell).
A cewar hukumar, gwajin wani bangare ne na kokarin Gwamnatin Jihar Kano na tabbatar da lafiyar ma’aurata da kare lafiyar jama’a yayin da ake ci gaba da shirin auren gata da aka tsara domin taimakawa al-ummar jihar masu karamin karfi.
Da yake tattaunawa da manema labarai yayin gwajin, Babban Darakta na KSACA, Dr Usman Bashir, ya ce ana gudanar da gwajin ne bisa ga Dokar Gwajin Lafiya Kafin Aure ta Jihar Kanod a aka kafa a 2024.
A cewarsa, dokar ta sa ya zama dole masu niyyar aure su yi gwajin cutar HIV, ciwon hanta, syphilis da sickle cell, da sauran gwaje-gwaje da kwararrun lafiya suka ga sun dace.
Dr Bashir ya bayyana cewa shirin daurin aure gaba daya yana daga cikin alkawuran da gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi na taimakawa mutanen da ba su da karfin biyan kudin daurin aure.
Babban jami’in KSACA ya ce an riga an fito da ma’aurata daga dukkan kananan hukumomi 44 na jihar ta hanyar tantancewa da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta yi, yayin da KSACA ke da alhakin gudanar da gwajin lafiya kamar yadda doka ta tanada.
Ya bayyana cewa hukumar ta riga ta gwada ma’aurata daga kananan hukumomi 23 da ba na cikin birni ba, kuma za ta ci gaba da sauran kafin ta kammala na kananan hukumomin birni.
A cewarsa, hukumar na fatan gwada akalla ma’aurata 150 wanda yayi daidai da mutane 300 a kowace rana, kuma sakamako yana shirin fitowa cikin awanni 24.
Dr. Bashir ya ce haka kuma ana yi wa mahalarta mata gwajin daukar ciki, yayin da za a gudanar da sauran gwaje-gwaje idan ma’aikatan lafiya suka yi zargin shan miyagun kwayoyi ko wasu matsalolin lafiya.
Ya kara da cewa ma’auratan da aka gano sun dace a bangaren lafiya za a ba su takardar shaidar aure, wadda za ta zama sharadi kafin shiga shirin daurin aure gata na gwamnati.
Dangane da sirri, DG ya tabbatar wa mahalarta cewa za a kiyaye bayanan lafiyarsu da sirri yadda ya dace.
“Za mu tuntubi wadanda abin ya shafa kai tsaye ta lambobin wayarsu, adireshi da sauran bayanan da muka karba. Wadanda aka gano suna dauke da cutar HIV kuma ba sa kan magani, za a tura su asibitoci kusa da inda suke zama don samun kulawa nan take,” in ji shi.
Ya bayyana cewa wadanda aka gano suna da ciwon hanta za a tura su yi karin gwaji, yayin da ma’auratan da ba su dace ta fannin jini ba saboda cutar sickle cell za a basu shawara kuma ba za a bar su ci gaba da shirin ba.
Ya bayyana gwajin a matsayin shiga tsakani na lafiyar jama’a da ke nufin rage matsalolin lafiya da za a iya hana yaduwarsu, musamman cutar sickle cell wadda ke ci gaba da shafar iyalai da dama.
Ya kuma jaddada cewa Gwamnatin Jihar Kano na gudanar da dukkan ayyukan gwajin kyauta.
A nasa bangaren, da yake yi wa manema labarai jawabi a yayin duba yadda aikin gwajin ke gudana, Kwamanda Janar na Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana gamsuwarsa da yadda ake gudanar da aikin.
“Mun ga yadda aka tsara abubuwa kuma mun gamsu cewa aikin yana tafiya yadda ya kamata,” in ji shi.
Daurawa ya lura cewa gwajin lafiya kafin aure ya kasance sharadi na doka don aure a Jihar Kano, kuma ya yaba wa KSACA bisa gudanar da aikin yadda ya kamata.
Ya ce Gwamna Yusuf ya bullo da shirin daurin auren gatan ne domin tallafa wa mata, marayu da sauran marasa karfi wadanda kan sami matsala wajen biyan kudin daurin aure.
A cewarsa, mutane da yawa ana tilasta musu su sayar da fili, gonaki, babur da sauran kayayyaki ko ma su rufa kudi don su yi aure.
Ya bayyana cewa masu cin gajiyar za su samu kayan daki, abinci, tufafi da sauran tallafi, yayin da kowace amarya za ta samu N200,000, wato N100,000 na sadaki da N100,000 na karfafa tattalin arziki.
Malamin ya roki masu cin gajiyar shirin su daraja aurensu su kuma rika mutunta juna, inda ya tabbatar musu cewa Hisbah za ta kafa kwamitoci don kula da tattaunawa, bukukuwan aure da rabon kayan tallafi.
Daurawa ya kara da cewa rahotannin da aka samu daga masu cin gajiyar shirin daurin aure na baya sun nuna an samu auratayya da yawa da haihuwa, yana mai kyakkyawan fata cewa shirin na 2026 zai samu nasara mafi girma.












































