Gwamnatin Jihar Kano ta fara gyaran Madatsar Ruwa ta Goron Dutse, babban kuma mafi muhimmancin wurin rarraba ruwa da ke hidima ga birnin Kano, a matsayin wani bangare na kokarin inganta samar da ruwan sha a fadin jihar.
Dr Dahir Muhammad Hashim, Kwamishinan Muhalli, Sauyin Yanayi da Albarkatun Ruwa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Litinin bayan kewayen duba ayyukan gyaran da ake ci gaba da gudanarwa a wurin.
A cewarsa, madatsar ta kunshi manyan tankuna uku na ajiyar ruwa da ke da karfin lita miliyan 7.3, lita miliyan 11.2 da lita miliyan 22.5, wanda hakan ya ba shi jimillar karfin ajiya na lita miliyan 40.5.

Hashim ya ce tankuna biyu kanana, wadanda ke da karfin lita miliyan 7.3 da lita miliyan 11.2, an gina su ne a shekarar 1930 amma an yi watsi da su fiye da shekaru 30.
Ya kara da cewa kusan dukkan muhimman abubuwan more rayuwa a tafkin an lalata su ne tsawon shekaru.
“Na yi farin cikin ganin cewa ayyukan gyara suna tafiya cikin tsari,” in ji shi.
Kwamishinan ya bayyana cewa ana ci gaba da sauya bututu a tankunan lita miliyan 7.3 da lita miliyan 11.2, yayin da ake cire laka a tankin lita miliyan 22.5 a yanzu.

Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya amince da wannan aikin a matsayin wani bangare na kokarin gwamnati na dawo da samar da ruwan sha a fadin Jihar Kano baki daya.
A cewar Hashim, gyaran Madatsar Goron Dutse da aikin da ake ci gaba da yi a Mataratar Tamburawa da Challawa da nufin inganta samar da ruwa da rarraba shi ga mazauna jihar.
Ya bayyana kwarin gwiwa cewa aikin zai karfafa ababen more rayuwa na ruwa a jihar kuma zai taimaka wajen magance matsalar rashin isasshen ruwa da Kano ta dade tana fuskanta.











































