Da ɗumi-ɗumi: An ga jinjirin watan Ramadan a Saudi Arabia

Crescent moon
Ramadan Kareem background with moon and stars, holy month. Elements of this image furnished by NASA nasa.gov

Rahotanni daga ƙasar Saudi Arabia sun tabbatar da cewa an ga jinjirin watan Ramadan domin fara watan mai alfarma.

A cewar Haramain, wata kafar yaɗa labarai da ke Saudiyya, bayan ganin jinjirin watan, hukumomin ƙasar za su ayyana ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026 a matsayin ranar farko ta watan Ramadan.

Tun da farko an sanar cewa za a gudanar da duban jinjirin watan a Hawtat Sudair da kuma Tumair a gundumar Al-Majma’ah.
Abdulaziz Al-Muainaa daga cibiyar lura da wata ta Al Hareeq ya ce, “Rana za ta fāɗi daidai ƙarfe 5:52 na yamma, kuma yanayin sararin samaniya ya dace domin ganin jinjirin watan Ramadan.”

Da yake sanar da ganin jinjirin watan a ranar Talata, Haramain ya ce, “An ga jinjirin watan a Saudiyya. Saboda haka, Ramadan 1447 zai fara daga daren yau.

A halin yanzu, Musulmi a Najeriya za su jira sanarwa kan fara Ramadan daga Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Amirul Muminina, Muhammad Sa’ad Abubakar na uku.

Ramadan shi ne wata na tara a kalandar Musulunci kuma mafi tsarki a shekara.

Ana tunawa da saukar da Alƙur’ani ga Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) a cikin sa ne ake dacewa da Lailatul Qadri, wadda ake yi a cikin kwanaki goma na ƙarshe na watan Ramadan.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here