Tinubu, Shettima sun gudanar da Sallar Idi a Abuja

Tinubu Shettima 1536x1152 1 750x430

A yau Lahadi ne shugaban kasa, Bola Tinubu ya bi sahun Musulmai a filin Sallar Idi na kasa da ke kan titin filin jirgin sama a Abuja, domin gudanar da Sallar Eid-el-Fitr da ke nuna karshen watan Ramadan

Tinubu wanda ya isa wurin ne da mintuna kadan kafin karfe tara na safe, ya samu tarba daga manyan jami’an gwamnati, malaman addini, da sauran manyan baki.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, na daga cikin wadanda suka halarci taron idin.

Karanta: Cikin Hotuna: Sarki Sanusi ya bukaci a hukunta wadanda suka kashe ’yan asalin Kano a Edo, ya bukaci matasa su guji daukar fansa

A ranar Lahadi da yamma, shugaban kasar zai karbi baki a fadar gwamnati a karon farko tun bayan hawansa karagar mulki domin cin abincin rana don bikin Eid-el-Fitr.

Karin karatu: Hotuna: Yadda aka gudanar da Sallar Idi a fadar Sarkin Kano da ke Nassarawa

Sannan ya gudanar da bukukuwan baya a gidansa na Ikoyi dak e Legas.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here