Wasu ‘yan majalisar tarayya biyu daga jihar Kano sun fice daga jam’iyyar (NNPP) sun koma jam’iyyar APC mai mulki, saboda rashin warware rikicin cikin gida a tsohuwar jam’iyyarsu.
SolaceBase ta ruwaito cewa Kabiru Alhassan Rurum mai wakiltar Rano/Bunkure/Kibiya da Abdullahi Sani Rogo na mazabar Karaye/Rogo sun bayyana sauya sheka a zaman da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas ya jagoranta a ranar Alhamis.
Sauye-sauyen nasu ya kara dagula yawan ‘yan majalisar da ke tsallakawa jam’iyyar APC a watannin baya-bayan nan. Oluwole Oke, dan majalisar wakilai daga jihar Osun, shi ma ya koma jam’iyyar APC a wannan zaman.
Taron dai ya samu halartan shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje da wasu jiga-jigan jam’iyyar, wadanda suka halarci taron domin tarbar sabbin mambobin jam’iyyar.
A cikin ‘yan watannin nan dai majalisar ta samu sauya sheka da dama, wanda da yawa daga cikinsu sun karkata ga jam’iyyar APC mai mulki













































