Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin Kasa ta’annati (EFCC) ta fara gudanar da bincike kan zargin cin hanci da rashawa da wasu manyan jami’an kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC Ltd) suka yi, wadanda suka hada da tsofaffin shugabannin biyu, Mele Kyari da Abubakar Yar’adua.
Wasikar mai lamba CR:3000/EFCC/ABJ/HQ/SDC.2/NNPC/VOL.1/698 mai dauke da kwanan watan 28 ga watan Afrilu zuwa ga Manajan Darakta na NNPC, ta nuna hukumar EFCC na neman takardun shaidar biyan albashi da alawus-alawus ga jami’ai 14 da suka hada da wadanda suka yi ritaya.
A cikin wasikar mai taken ‘bukatar ayyukan bincike don samun bayanai’, EFCC ta ce tana gudanar da bincike kan laifin cin zarafin ofis da kuma almubazzaranci da kudade, ta kuma bukaci kamfanin da ya samar da sahihan takardu na gaskiya da ya kunshi ma’aikata na yanzu da na baya.
Karin karatu: Tinubu ya cire Mele Kyari daga shugabancin NNPCL
Daga cikin sunayen da aka lissafa akwai tsohon shugaban kamfanin Mele Kyari; tsohon Manajan Daraktan Kamfanin (PHRC), Ibrahim Onoja; da tsohon Manajan Daraktan Kamfanin (KRPC), Mustafa Sugungun.
An cire dukkan mutanen uku ne a wani rikici da ya barke a kamfanin man.
Sauran da ke cikin jerin sunayen sun hada da: tsohon Manajan Darakta na Kamfanin NNPC, Abubakar Yar’Adua; tsohon babban daraktan kamfanin NNPC, sashin kudi da ayyuka Isiaka Abdulrazak, tsohon babban jami’in kudi na NNPC, Umar Ajiya, tsohon Manajan Darakta na PHRC, Dikko Ahmed Injiniya mai samar da wutar lantarki a PHRC, Ademoye Jelili, Manaja samar da mai a NNPC/KRPC, Efiok Akpan, Kayode Adetokunbo, Babatunde Bakare, Jimoh Olasunkanmi, Bello Kankaya da Desmond Inyama.
Binciken dai yana da nasaba da bacewar dalar Amurka biliyan 2.896 mai cike da cece-kuce da aka kashe kan ayyukan gyaran matatun da ke karkashin su.
Karanta: Sabon shugaban kamfanin NNPCL Ojulari ya karbi aiki daga hannun Kyari
Daga cikin wannan kudi an ware dala biliyan 1.56 ga matatar mai ta Fatakwal, da dala miliyan 740.6 ga matatar mai ta Kaduna, da kuma dala miliyan 656.9 ga matatar mai ta Warri.
Lokacin da PREMIUM TIMES ta tuntubi kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da cewa ana ci gaba da binciken amma ya ce bai da cikakken bayani.
A ranar Laraba ne PREMIUM TIMES ta kawo rahoton korar manajan daraktocin matatun mai uku.
Wata majiya da ke da masaniya kan lamarin ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa, an cire Manajan Darakta na Kamfanin mai na Fatakwal (PHRC), Ibrahim Onoja da Manajan Daraktan Kamfanin mai na Warri (WRPC), Efifia Chu, da Manajan Daraktan Kamfanin mai na Kaduna Mustafa Sugungun.
Ya ce tsigewar wani bangare ne na yin gyara a kamfanin ba wai wani yunkuri ne na korar magoya bayan tsohon shugaban kamfanin ba.
A watan da ya gabata ne shugaban kasa Bola Tinubu ya kori shugabannin kamfanin NNPC da suka hada da GCEO Mista Kyari da shugaban hukumar Pius Akinyelure.
Shugaban ya kuma amince da Bayo Ojulari a matsayin sabon shugaban NNPC da Ahmadu Kida a matsayin wanda ba shugaban kasa ba.
Kamfanin NNPC ya kuma bayyana nadin sabbin manyan jami’an gudanarwar mai mutum 8.
A makon da ya gabata, Ministan Kudi na Najeriya kuma Ministan Tattalin Arziki, Wale Edun, ya sanar da cewa ana gudanar da binciken kwakwaf na kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC) a wani taron masu zuba jari da aka gudanar a gefen taron Bankin Duniya/IMF da aka gudanar a birnin Washington, D.C.