Jam’iyyar APC ta fitar da jerin sunayen ‘yan takarar Sanatan da ba a amince su shiga zaben fidda gwanin jam’iyyar ba.
An fitar da jerin ne a ranar Litinin a cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labaran jam’iyyar na Kasa, Felix Morka, ya fitar.
A cewar sanarwar, “Jam’iyyar APC ta fitar da jerin sunayen ‘yan takarar Sanatan da ba a amince su shiga zaben fidda gwanin jam’iyyar ba.
“Kwamitocin Tattara Bayanai na jam’iyyar ne suka gudanar da aikin tantancewa bisa tsari da ka’idojin da aka gindaya.”
Cikakken bayani nan ba da jimawa ba…












































