Mafarauta Da Yan Banga Sun Kashe ‘Yan Bindiga 30 a Jihar Taraba

C32E642C CBFE 483F 87CE A35984E10D16 w1023 r1 s
C32E642C CBFE 483F 87CE A35984E10D16 w1023 r1 s

Kungiyar hadin gwiwa ta mafarauta da yan banga na ci gaba da samun nasara a fafatawar su da ‘yan bindiga masu tayar da kayar baya a jihar Taraba.

Yayin da rashin zaman lafiya ke ci gaba da addabar wasu yankunan arewacin Najeriya, wasu al’umomi a jihar Taraba sun dauki matakin shawo kan lamuran tsaro, ta hanyar hada taro da sisi don daukar nauyin mafarauta sun tunkari lamarin.

Jihar Taraba na daya daga cikin jihohin dake fama da matsalar ‘yan bindiga dake kai wa al’umomin yankunan hare-hare, baya ga haddasa asarar rayuka, su kan kwashi dukiya ko barnatawa tare da yin garkuwa da mutane domin kudin fansa.

A yunkurin neman dawo da zaman lafiya kungiyar hadin gwiwar mafarauta da ‘yan banga, an sama da ‘yan bindiga talatin a yankin Garbabi dake karamar hukumar Gashaka a jihar Taraba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here