Gwamnatin jihar Edo, ta ce ta kama sarakun guda biyu tare da wasu mutum biyar waɗanda ake zargi da hannu a garkuwa da fasinjoji 20 a hari kan tashar jirgin ƙasa a jihar ranar 7 ga watan Janairu.
Kwamishinan sadarwa da wayar da kai a jihar, Chris Nehikhare, shi ya bayyana hakan jiya a Benin yayin zantawa da manema labarai jim kadan bayan fitowa taron majalisar zartaswa.
Ya ce jami’an tsrao sun samu nasarar kuɓutar da mutum biyu da suka rage a hannun masu garkuwa da mutanen.
A ranar 7 ga watan Janairu ne, wasu da ake zargin ‘yan bindiga suka kai hari tashar jirgin ƙasa a jihar tare da sace mutum 20.












































