Shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya sake nanata cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar kisa da yawa, yana mai cewa waɗannan hare-haren suna zama barazana ga ci gaban Kiristanci a ƙasar.
A cikin wani faifan bidiyo da fadar White House ta wallafa a shafin X a ranar Laraba, Trump ya ce, dubban Kiristoci ake kashewa, yana zargin “’yan ta’addan Musulmai” da aikata wannan abin da ya kira kisan gilla.
A cikin faifan, Trump ya sanar da cewa ya sanya Najeriya cikin jerin “ƙasashe na musamman da ake damuwa da su,” bisa ga ƙa’idar doka da gwamnatin Amurka ta tanada.
Ya ce idan aka ci gaba da kisan Kiristoci ko wata ƙungiya makamanciya, hakan ya zama abin da bai dace ba kuma yana buƙatar gaggawar daukar mataki daga majalisar dokoki ta Amurka.
Trump ya bayyana cewa alkaluman da ke nuna adadin waɗanda aka kashe abin takaici ne, don haka ya bukaci majalisar dokoki ta Amurka da ta binciki lamarin cikin gaggawa.
Ya ce ba za a iya bari irin wannan kisa ya ci gaba da faruwa ba yayin da Amurka ke kallo kawai.
Ya ce Amurka za ta ɗauki mataki wajen kare al’ummar Kirista a duniya domin wannan lamari ba zai ci gaba da faruwa ba.
Trump ya taɓa yin barazanar tura ma’aikatar yaƙin Amurka zuwa Najeriya idan har kisan Kiristoci bai tsaya ba.
Ya kuma tabbatar da cewa ya riga ya sanya Najeriya cikin jerin “ƙasashe na musamman da ake damuwa da su” saboda waɗannan zarge-zargen.
Rahoton ya nuna cewa wannan ƙayyadadden matsayi na “ƙasa ta musamman da ake damuwa da ita” yana nufin ƙasa da gwamnatin Amurka ke kallon tana aikata abubuwan da ke barazana ga haƙƙin ɗan adam.
Wannan matsayi yawanci ana ɗauka ne a ƙarƙashin doka ta musamman da sakataren harkokin wajen Amurka ke amfani da ita.
A gefe guda, gwamnatin tarayya ta Najeriya ta bayyana cewa ƙasar na ci gaba da kasancewa ƙasa mai tsarin dimokuraɗiyya wacce ke ba da cikakken ’yancin addini ga dukkan ’yan ƙasa.
A wata sanarwa daga shugaban ƙasa Bola Tinubu a ranar 1 ga Nuwamba, ya ce Najeriya ƙasa ce da ke tafiya bisa kundin tsarin mulki mai tabbatar da ’yancin yin addini, kuma gwamnati na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai wajen magance matsalolin tsaro a dukkan yankuna.
Tinubu ya ƙara da cewa yadda ake ɗaukar Najeriya a matsayin ƙasa mai nuna bambancin addini ba ya wakiltar ainihin halin da ƙasar ke ciki, domin ’yancin yin addini da juriya sun kasance ginshiƙai na haɗin kan al’ummar Najeriya tun fil azal.













































