Tinubu ya karɓi shaidarsa ta cin zaɓe

334545325 151271951133905 4030527573900318743 n
334545325 151271951133905 4030527573900318743 n

Hukumar zaɓen Najeriya ta miƙa wa zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu shaidar cin zaɓen 2023.

Shugaban Hukumar Zaɓen Ƙasar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya miƙa masa shaidar a Abuja.

Haka ma, shugaban na INEC ya bai wa mataimakinsa Kashim Shettima, shaidarsa.

An danka musu takardar shedar ne sa’o’i kalilan bayan da INEC ta ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara a zaben ranar Asabar 25 ga watan Fabarairun 2023, inda ya samu kuri’a 8, 794, 726, da suka ba shi galaba a kan sauran ‘yan takara 17.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here