Hukumar zaɓen Najeriya ta miƙa wa zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu shaidar cin zaɓen 2023.
Shugaban Hukumar Zaɓen Ƙasar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya miƙa masa shaidar a Abuja.
Haka ma, shugaban na INEC ya bai wa mataimakinsa Kashim Shettima, shaidarsa.
An danka musu takardar shedar ne sa’o’i kalilan bayan da INEC ta ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara a zaben ranar Asabar 25 ga watan Fabarairun 2023, inda ya samu kuri’a 8, 794, 726, da suka ba shi galaba a kan sauran ‘yan takara 17.













































