Shugaba Bola Tinubu ya fara hutun shekara na makonni uku.
Bayanin hakan na cikin wata sanarwar Babban Mataimakin Shugaban Kasa kan Yada Labarai da Dabarun, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.
Sanarwar ta ce Tinubu zai bar Abuja a ranar Lahadi (yau) zuwa Turai, inda zai tsaya a London, Birtaniya.
A cewar sanarwar, ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo gida bayan hutun nasa na aiki, domin ya shiga yakin neman zabe mai zafi na zaben Janairu 2027.












































