Tinubu ya fara hutun shekara na makonni uku, ya tashi zuwa Turai

Tinubu depart new

 

Shugaba Bola Tinubu ya fara hutun shekara na makonni uku.

Bayanin hakan na cikin wata sanarwar Babban Mataimakin Shugaban Kasa kan Yada Labarai da Dabarun, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce Tinubu zai bar Abuja a ranar Lahadi (yau) zuwa Turai, inda zai tsaya a London, Birtaniya.

A cewar sanarwar, ana sa ran Shugaba Tinubu zai dawo gida bayan hutun nasa na aiki, domin ya shiga yakin neman zabe mai zafi na zaben Janairu 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here