Tinubu da Kwankwaso sun shirya wata muhimmiyar ganawa a fadar Aso Villa

Kwankwaso and Tinubu

Ana sa ran shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi wata muhimmiyar ganawa da jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a fadar shugaban ƙasa ta Aso Villa, lamarin da ke nuna sabon salo a rikicin siyasar jihar Kano da ke ci gaba da ɗaukar hankalin jama’a.

Wannan shiri na ganawa ya biyo bayan wata ganawar sirri ta musamman da shugaban ƙasa ya yi da gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ake ɗauka a matsayin amintaccen abokin siyasa na Kwankwaso, a ranar Litinin.

Majiyoyi sun bayyana cewa gwamna Abba Kabir Yusuf ya taka muhimmiyar rawa wajen sauƙaƙa wannan shiri, bayan da shugaban ƙasa ya nuna buƙatar daidaita muhimman muradun siyasa tsakanin jam’iyyu daban-daban, a matsayin wani ɓangare na shawarwari da ake yi gabanin zaɓen 2027.

A baya-bayan nan, Sanata Kwankwaso ya kasance mai tsauraran ra’ayi kan ƙin shiga jam’iyyar APC, tare da nuna rashin amincewa da yiwuwar gwamnan Kano ya sauya sheƙa.

Sai dai a ‘yan makonnin nan, matsayinsa ya fara sassautawa a idon jama’a.

A wata tattaunawa da ya yi da manema labarai, tsohon gwamnan Kano kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, ya nuna yiyuwar sake tsara matsayinsa na siyasa idan aka gabatar masa da tayin da ya gamsar da shi daga jam’iyyar mai mulki.

Wani babban jigo a jam’iyyar APC daga yankin Arewa maso Yamma ya tabbatar da cewa an tsara taron tsakanin shugaban ƙasa da Sanata Kwankwaso a yau, sai dai yana iya sauyawa dangane da jadawalin ayyukan shugaban ƙasa, inda ake sa ran tattaunawar za ta ta’allaka ne kan zaman lafiyar ƙasa, haɗin kan siyasa da kuma yadda za a tsara karfi gabanin zaɓen 2027.

Masana siyasa na ganin cewa duk wata yiwuwar haɗuwar tafiyar Kwankwasiyya da APC za ta haifar da gagarumin sauyi a siyasar Arewacin Nijeriya, tare da ƙarfafa matsayin APC a jihar Kano, wadda ake kallon ta a matsayin muhimmin filin fafatawa a zaɓukan ƙasa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here