Shahararren mawaƙin Yarabawa, kuma marubuci, Olanrewaju Adepoju ya rasu yana da shekaru 83 a duniya.
Ya rasu ne da misalin karfe 7:00 na yammacin ranar Lahadi a gidansa da ke Ibadan, jihar Oyo.
Ɗansa, Adejare Adepoju ne ya sanar da rasuwarsa a yammacin Lahadi.
Wasu daga cikin wakokinsa sun hada da Sagba Dewe, Ironu Akewi, Orirun Yoruba, da sauransu.
A zamanin mulkin Soja, Adepoju ya kasance mai karfin gaske domin yawancin wakokinsa sun ta’allaka ne kan gyara matsalolin al’umma da manufofin gwamnati marasa kyau.













































