Sarkin Lokoja ya rasu yana da shekara 80

Collage Maker 29 Sep 2022 06.56 AM 1024x1024 1
Collage Maker 29 Sep 2022 06.56 AM 1024x1024 1

Daya daga cikin manyan sarakunan Najeriya, Maigari na Lokoja, Alhaji (Dr) Muhammad Kabir Maikarfi lll ya rasu.

Maigari, mai shekaru 80, ya rasu da yammacin jiya Laraba bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Abuja.

Ya kasance ɗaya daga cikin sarakunan gargajiya mafi dad6ewa a jihar Kogi, inda ya hau karagar mulki a 1992.

Sakataren Majalisar Gargajiya na karamar hukumar Lokoja, Muhammed Nalado Usman ya tabbatar da rasuwar basaraken a wata sanarwa da ya fitar a daren jiya Laraba.

Sanarwar ta ce za a yi jana’izar marigayin a yau Alhamis a Lokoja da karfe 4 na yamma.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here