Kwamishinan ‘yan sanda a jihar Sakkwato Muhammad Usaini Gumel, yace sun samu labarin ana tara makaman ne inda suka kai samame suka kama makamai a ofisoshin jam’iyun APC da PDP na karamar hukumar Isa.
Yace makaman sun hada da adduna, sanduna, bindigar gargajiya ta harba ruga da sauran nau’o’in makamai.
To sai dai Muryar Amurka ta tuntubi kakakin jam’iyun da aka kama makaman a ofisoshin su, sun ce ba su da masaniyar haka.
Wannan na zuwa ne lokacin da rundunar sojin Najeriya ta ce tayi shiri na taimakawa a gudanar da zabe cikin lumana.
Tuni jama’ar yankunan da ke fama da matsalar rashin tsaro su ka nuna fargaba abin da kan iya faruwa lokutan zabe.












































