Rashin Tsaro: Har ila yau, FRSC na neman izinin gwamnatin tarayya akan ɗaukar makamai

0

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta ce akwai bukatar jami’anta su rike makamai wajen gudanar da ayyukansu, duba da irin kalubalen tsaro da ake fuskanta a fadin kasar nan. Shugaban rundunar, Mista Dauda Biu ne ya bayyana haka a ranar Asabar a lokacin da yake kaddamar da jami’an rundunar su 1,762 da suka kammala karatunsu na tsawon watanni hudu a cibiyar horas da sojojin Najeriya (NATRAC) da ke Kontagora a Nijar.

Idan dai za a iya tunawa, a baya rundunar ta kai karar jami’anta da su dauki makamai domin kare lafiyarsu, kiran da hukumomi suka yi watsi da shi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here