Kwamitin Ba da Gata ga Masu Aikin Lauya LPPC ya zabi Sagir Gezawa Suleiman, Mas’ud Mobolaji Alabelewe da sauran lauyoyi 75 tare da Farfesa Ahmed Rabiu da Farfesa Ibrahim Abikan Abdulqadir da sauran malamai 10, domin ba su matsayin Babban Lauyan Najeriya (SAN) mai daraja a shekarar 2026.
SolaceBase ta ruwaito cewa an sanar da sunayen da aka zabna a cikin wata sanarwa da Sakataren LPPC kuma Babban Rijistaran Kotun Kolin Najeriya, Kabir Eniola Akanbi ya fitar a ranar Talata, bayan kammala bin manyan matakai a tsarin zaben.
A cewar kwamitin, wadanda aka zaba sun ci jarrabawar Tantance Masu Kare Shari’a, Jarrabawar Tantance Malamai, sauraron kara mai zaman kantas da kuma aikin ofisoshi, wanda ya basu damar kaiwa ga matakin tantancewa na tsarin ba da matsayin SAN.
Daga cikin wadanda aka zaba a rukunin lauyoyin akwai Jude Chukwuemeka Okafor, Godwill Achebong Umoheso, Sunday Samuel Obende, Adebayo Olugbenga Adaralegbe, Jimson Ejovi Okodaso, Sagir Gezawa Suleiman, Mas’ud Mobolaji Alabelewe, Aisha Ado Abdullahi, Faruk Abdullahi, Mohammed El-Hassan Sheriff, Junaidu Bello Marshall da sauran su.
A rukunin malaman jami’a, kwamitin ya zabi farfesoshi 12, ciki har da Farfesa John Alewo Musa Agbonika, Farfesa Najeem Adeyemi Ijaiya, Farfesa Nnamdi Onyeka Obiaraeri, Farfesa Nathaniel Ahabue Inegbedion, Farfesa Akkarren Samuel Shaakaa, Farfesa Olusesan Luqaid Oliyide, Farfesa Violet Omon Aigbokhaevbo, Farfesa Emmanuel Ayangarumun Kenen, Farfesa Collins Obioma Chijioke, Farfesa Ahmed Rabiu, Farfesa Ibrahim Abikan Abdulqadir da Farfesa Omoniyi Bukola Akinola.
LPPC ta gayyaci jama’a da su bayyana ra’ayoyi kan mutunci, kima da kwazo na wadanda aka zaba.
Ta ce dole ne kowani korafi ya kasance tare da cikakkiyar shaidar da aka rantse a gaban Babbar Kotun a Najeriya ko kuma aka yi a gaban ofishin kotun koli.
Kwamitin ya kara da cewa dole ne a mika kwafi 20 na irin wadannan kararraki ga ofishin Sakataren LPPC kafin karfe 4 na yamma ranar 15 ga Yuli 2026, ko kuma a aika ta adireshin imel na kwamitin.
Duk da haka, kwamitin ya jaddada cewa wallafa sunayen wadanda aka zaba ba yana nufin an yi nasara ba, inda ya cewa duk wadanda aka sanar dole ne a tantance su kafin a yanke hukunci na karshe.
Matsayin SAN shi ne mataki mafi girma ga masu aikin lauyanci a Najeriya kuma ana ba da shi kowace shekara ga lauyoyi da malaman jami’a da suka nuna kwarewa da ba da gudummawa wajen bunkasa fannin lauyanci.













































