
Mai alfarma sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya bayyana fargabar cewa Najeriya na fuskantar barazanar tsaro bisa la’akari da yadda dumbin matasan kasar nan ke fama da rashin aikin yi da yunwa.
Sarkin Musulmin ya yi wadannan kalamai ne yayin da yake jawabi a wani taron majalisar sarakunan gargajiya ta arewacin Najeriya ranar Laraba a Kaduna.
Karanta wannan: An rantsar da Douye Diri a matsayin gwamnan Bayelsa a wa’adi na 2
Muhammad Sa’ad Abubaakr III ya ce “Mun shiga wani sabon zango na shugabanci. An samu sabbin gwamnoni inda kuma wasu suka yi tazarce a karo na biyu amma har yanzu muna fama da matsalar tsaro.
Babban matsalar ma ita ce karuwar talauci. Mafi yawancin mutanenmu ba su da hanyoyin samun abin da za su ci su sha”.
Ya kara da cewa idan dai har gwamnoni na son zaman lafiya a jihohinsu, dole ne su samawa matasa aikin yi sannan dole ne su yi aiki tare da sarakunan gargajiya.
Karanta wannan: ‘Yan sanda sun kama mutum 400 da ake zargi da aikata laifuka a Legas
“Dole ne mu samawa dimbin matasanmu masu zaman kashe wando ayyukan yi. Na sha fadar cewa muna wasa da bakin wuta.
Saboda samun miliyoyin matasa ba tare da ayyukan yi ba sannan suna fama da yunwa, hakan na nufin muna fuskantar barazana.”
Daga karshe ya ce ya yi amannar cewa za’a samu mafita duk da cewa “Najeriya ba ta taba gaza samar da mafita ba illa dai kawai ba’a iya aiwatarwa”.










































