Kungiyar lauyoyin Najeriya NBA ta yi karin haske kan cewa Naira miliyan 300 da ta karba daga hannun gwamnatin jihar Rivers kyauta ce da ba za a iya mayarwa ba, ba wai ta biya hakkin daukar nauyin babban taronta na shekara-shekara ba.
A baya dai kungiyar ta NBA ta mayar da taron da ke tafe zuwa jihar Enugu bayan ayyana dokar ta baci a Rivers.
A martanin da gwamnatin jihar Ribas ta yi a ranar Litinin din da ta gabata, ta bukaci a maido da makudan kudin har miliyan 300.
Labari mai alaƙa: Ku dawowa da Jihar Rivers Naira miliyan 300 na karbar bakuncin babban taron shekara -Ibas ya fadawa NBA
NBA, a cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin tsare-tsare na AGC 2025, Emeka Obegolu SAN ya fitar, ya ce: “An jawo hankalin kwamatin tsare-tsare na babban taron shekara-shekara kan wata sanarwa da mai kula da jihar Rivers ya fitar kan yadda gwamnatin jihar ta biya hakkin karbar bakuncin NBA na 2025.
Idan ba a manta ba, a ranar Asabar din da ta gabata ne kungiyar NBA ta bayyana cewa, matakin da babban jami’in gwamnatin jihar Rivers, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) ya yi, ya gurgunta cibiyoyi da tsarin dimokuradiyya.
A cewar NBA, Ibas yana gudanar da aiki ba tare da la’akari da tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma kararrakin da ake ci gaba da yi ba.










































