Masu kallon ƙwallon ƙafa daga Senegal 18 da aka tsare a Maroko kan wasan AFCON sun shiga yajin aikin cin abinci

senegal vs morocco fans 750x430

Masu kallon ƙwallon ƙafa daga Senegal su 18 da aka tsare a ƙasar Maroko bisa zargin tayar da tarzoma a lokacin wasan ƙarshe na gasar kofin ƙwallon ƙafa na Afirka AFCON da aka buga a watan da ya gabata, sun fara yajin aikin cin abinci har zuwa lokacin shari’arsu, a cewar lauyansu a ranar Juma’a.

Lauya Patrick Kabou ya bayyana cewa mutanen da yake karewa sun shaida masa cewa tun ranar 18 ga Janairu suke jiran a bayyana musu tuhumar da ake yi musu, ranar da aka kama su bayan wasan ƙarshe mai cike da tashin hankali inda Senegal ta doke Maroko a birnin Rabat.

Kabou ya ce ƙungiyar ta koka da cewa jami’an ’yan sanda sun yi musu tambayoyi ne da harshen Faransanci da Larabci, alhali su ba sa jin waɗannan harsuna, domin harshensu na asali shi ne Wolof.

Kafin mintuna kaɗan a ƙare wasan na watan da ya gabata, wasu magoya bayan Senegal sun yi yunƙurin kutsa kai cikin fili, yayin da ’yan wasan Senegal suka dakatar da wasan na kusan mintuna 20 domin nuna adawa da bugun fanareti da aka bai wa Maroko a ƙarshen wasa.

An kuma ga wasu magoya baya suna jefa abubuwa cikin fili, ciki har da kujera.

Ƙungiyar ta ce ana tauye musu haƙƙinsu na samun adalci, tare da alƙawarin ci gaba da yajin aikin cin abincin har sai kotun Maroko ta ba su damar a saurare su, a cewar Kabou.

Kotun farko da aka shirya a ƙarshen watan Janairu alƙali ya ɗage ta, haka kuma zaman kotu na biyu da aka shirya a ranar Alhamis ya samu ɗagawa sakamakon yajin aikin lauyoyi da ake yi a Maroko.

An tsara ci gaba da shari’ar a mako mai zuwa.

AFP.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here