Shettima ya dawo Abuja bayan halartar taruka a Guinea da Switzerland

Shettima Arrival (1)

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya dawo Abuja a ranar Asabar bayan kammala wasu muhimman ayyuka na diflomasiyya da tattalin arziki da ya gudanar a ƙasashen Guinea-Conakry da Switzerland.

Shettima ya sauka a filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, bayan ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da sabon Shugaban Ƙasar Guinea Mamadi Doumbouya.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa NAN ya ruwaito cewa Mataimakin Shugaban Ƙasar ya kuma jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron shekara-shekara karo na 56 Mai taken World Economic Forum WEF, wanda aka gudanar a birnin Davos na ƙasar Switzerland.

A cewar Shettima, ziyarar ta kasance wani ɓangare na sabunta ƙudirin Najeriya na ƙarfafa haɗin kai a yankin Yammacin Afirka, tare da yunƙurin sake farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa a ƙarƙashin shirin Shugaba Tinubu na “Renewed Hope”.

Daga cikin muhimman abubuwan da suka fito a Davos akwai ƙaddamar da Nigeria House, wadda ta kasance rumfar ƙasa ta farko ta Najeriya a tarihin WEF, wadda aka tsara a matsayin cibiyar dindindin ta jawo jarin zuba hannun jari a fannoni kamar ma’adinai, noma da tattalin arzikin dijital.

Haka kuma, Shettima ya haɗa kai da tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo, da Ministan Kuɗi, Wale Edun, wajen haɓaka shirin Accra Reset Initiative, wanda ke ƙarfafa masana’antu a Afirka bisa dogaro da jarin cikin gida da sarkar daraja, maimakon dogaro da tallafin ƙasashen waje.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here