Kungiyar kwallon kafa ta Man City ta samu tikitin kaiwa ga wasan karshe a gasar cin kofin zakarun nahiyar turai ta shekarar 2023, bayan da ta yi wa Real Madrid dukan kawo wuka.
Awasan farko da aka buga tsakanin manyan kungiyoyin 2, an tashi 1-1, yayin da akaro na biyu Man City ta jefa kwallaye 4 babu ko daya a filin wasa na Etihad dake England.
Ayanzu haka wasan karshe zai kasance tsakanin Manchester City da Inter Milan a birnin Istanbul na kasar Turkiya













































