Tsohon mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Hakeem Baba Ahmed, ya bayyana cewa jam’iyyar ADC na iya fuskantar rarrabuwar kai mai tsanani idan tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a babban zaɓen da ke tafe.
Baba Ahmed ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi a tashar talabijin ta Channels, inda ya yi bayani kan yanayin siyasa a cikin jam’iyyar ADC da kuma burin manyan ‘yan siyasar da ke cikinta.
A cewarsa, Atiku Abubakar na da matsayi mai ƙarfi na fitowa a matsayin ɗan takarar jam’iyyar ADC idan aka gudanar da babban taron jam’iyyar na ƙasa, lamarin da ya ce zai janyo ficewar wasu ‘yan takara da magoya bayansu da ba su gamsu da sakamakon ba.
Ya yi nuni da cewa jam’iyyar ADC a halin yanzu tana ɗauke da fitattun ‘yan siyasa masu burace-burace iri daban-daban, kuma da zarar an fara zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa, rikici da sabani za su bayyana fili.
Baba Ahmed ya kuma tabo matsayar tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, yana cewa salon siyasarsa bai dace da tsarin fafatawa a zaɓen fidda gwani na jam’iyya ba, saboda yana da ra’ayin tsayawa kai tsaye a matsayin ɗan takara ba tare da fafatawa da wasu ba.
Ya ƙara da cewa Peter Obi ya saba samun amincewar jam’iyya a matsayin ɗan takarar da aka haɗa kai a kansa, ba tare da tsauraran gasar cikin gida ba, lamarin da ka iya ƙara tsamin dangantaka a cikin jam’iyyar ADC idan aka shiga tsarin zaɓen fidda gwani.
A cewar Baba Ahmed, duk waɗannan abubuwa na nuna cewa idan Atiku Abubakar ya samu tikitin jam’iyyar ADC, akwai yiwuwar manyan mambobi da magoya baya su fice, abin da zai iya girgiza haɗin kan jam’iyyar da makomarta a fagen siyasar ƙasa.













































