Mahaifiyar Gwamnan Ondo ta rasu

Akeredolu and late mother
Akeredolu and late mother

Mahaifiyar Gwamnan Jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, Uwargida Grace Akeredolu ta rasu.

Babban Sakataren Yada Labaran Gwamnan dMista Richard Olatunde ya tabbatar da rasuwar a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce marigayiyar ta rasu “lafiya a cikin lokacin barcinta da sanyin safiyar yau Alhamis tana da shekaru 90.

Sanarwar ta ce “Ta rasu ta bar ‘ya’yanta, jikoki da sauran ‘yan uwa, Kuma nan gaba kadan za a fitar sabuwar sanarwa”

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here