Gwamnan jihar Anambra, Chukwuma Soludo, ya ce kusan dukkan wadanda ake zargi da aikata laifuka da aka kama a jihar cikin shekaru uku da suka gabata ‘yan kabilar Igbo ne.
Soludo ya yi wannan tsokaci ne a yayin wani taro da ‘yan asalin jihar Anambra mazauna kasashen waje suka shirya, wanda aka gudanar a otal din Metro Points da ke New Carrollton, Maryland, Amurka.
Gwamnan ya ce tun da farko ya yarda da labarin cewa makiyaya ne ke haddasa tashe-tashen hankula da aikata laifuka a sassan Kudu maso Gabas.
“Na yi mulki tsawon shekaru uku da wata uku, idan muka kama masu laifi 100 da masu garkuwa da mutane, kashi 99.99% na matasan Igbo ne,” in ji gwamnan.













































